Jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya ta gode wa ‘yan ƙasar saboda zaɓar dan takararsu Bola Tinubu a zaɓen da aka gudanar a ranar Asabar.
Tinubu da ake gani a matsayin gogaggen ɗan siyasa wanda kuma ke da shekara 70, ya samu kuri’u kusan miliyan tara.
Rabon da a yi fafatawa mai zafi a zaɓen Najeriya shi ne tun lokacin da ƙasar to dawo mulkin dimokuraɗiyya a 1999.
“Mun gode wa ‘yan Najeriya saboda zaɓar Bola Ahmed Tinubu, a matsayin shugaban Najeriya,” in ji jam’iyyar a wani sako da ta wallafa a shafin twita.