fidelitybank

Mun gano Ɗalibai 3,000 da suka kammala jami’a ta bogi – JAMB

Date:

Hukumar shirya jarabawar shiga makarantun gaba da sakandire ta ƙasa (JAMB), ta bankaɗo daliban da suka kammala karatun jami’a na bogi 3,000 da kuma mallakar takardun shaidar kammala karatu ba bisa ƙa’ida ba a duk faɗin ƙasar.

Magatakardar hukumar, farfesa Ishaq Oloyede ne ya bayyana hakan kuma ya ce waɗannan mutane ba su taɓa zuwa jami’a ba, wanda hakan ya nuna irin cin hanci da rashawa da ake samu a harkar ilimi.

Oloyede ya soki yadda wasu cibiyoyin karatu suke shigar da ɗalibai makarantu ba bisa ƙa’ida ba, yana mai cewa abin kunya ne ga al’ummar ƙasar.

Ya kuma buƙaci kwamitin Pro-Chancellor na Jami’o’in Jihohi a Najeriya (COPSUN) da su yaƙi irin waɗannan ayyuka.

A watan Disamban 2023, Kwamitin Majalisar Wakilai kan Ilimin Farko ya buƙaci Hukumar JAMB ta samar da jerin sunayen cibiyoyin da ke da hannu wajen shigar da ɗaliban jami’o’i ba bisa ƙa’ida ba.

A shekarar da ta gabata ne kuma JAMB ta ba da shawarwari kan hanyoyin da za a bi don gano yadda ake shigar da mutane jami’o’i ba bisa ƙa’ida ba.

Tun da farko dai hukumar jarabawar ta gargaɗi masu neman gurbin karatu da su daina karɓar damar samun karatu da irin waɗannan cibiyoyi ke yi ba tare da cikakken halartar jarabawa da ƙa’idojin shiga jami’a ba.

Hukumar JAMB ta kuma mayar da martani ga ƙorafin da aka yi a kafafen sada zumunta game da tsarin daidaita jarabawa, inda ta ce dole ne duk waɗanda suka rubuta jarabawar su bi ta JAMB domin kaucewa kura-kurai.

Oloyede ya lura cewa daga shekarar 2017 zuwa 2020, cibiyoyin karatu a Najeriya sun gudanar da shigar da sama da ɗalibai 706,000 jami’o’i ba bisa ƙa’ida ba, da gurɓata kididdigar rajista na kasa da kuma karya manufofin ilimi.

nan news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp