Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta INEC, ta bayyana gamsuwarta game da yadda mutane ke fitowa domin karɓar katin zaɓe da hukumar ke rabawa a fadin ƙasa.
Babban kwamishina a hukumar zaɓen kuma shugaban kwamitin yaɗa labarai da ilimantar da masu kaɗa ƙuri’a, Festu Okoye ne ya bayyana haka a wata zantawa da gidan talbijin na Channels.
Mista Okoye ya dangata fitowar jama’a da yadda shugabanni a matakai daban-daban ke wayar da kan jama’a game da fitowa karɓar katin zaɓen.
“Yawan ƙarbar katin ya bambanta daga wannan jiha zuwa waccan, kuma muna samun bayanai daga kwamishinoninmu da ke jihohin ƙasar daban-daban”, kamar yadda ya bayyana.
Haka kuma babban kwamishin a hukumar ya ce hukumar na fuskantar matsaloli game da mutanen da ba su san hanyar za su bi domin karɓar katin nasu ba.
INEC ta karbi kashin karshe na BVAS
Ya ce, INEC ba za ta buga katin ga mutanen da suka yi rajista fiye da sau ɗaya ba, saboda a cewarsa har yanzu tsoffin katinsu yana aiki.
Amma ga waɗanda suka sauya wurin gudanar da zaɓe, za su iya samun katinan nasu a wuraren da ake karɓar katin.