fidelitybank

Mun gaji bashin biliyan goma sha uku na ‘yan fansho – Gwamnatin Zamfara

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta gaji sama da Naira biliyan goma sha uku na kudaden fansho da baratu daga gwamnatocin baya.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a ranar Larabar da ta gabata yayin bikin cikar sa shekara guda a Gusau babban birnin jihar.

A cewarsa, tun daga lokacin mulkinsa zuwa yau, ya daidaita sama da Naira biliyan 5 na kudaden fansho da garatuity.

“Na gaji sama da Naira biliyan goma sha uku fansho da koma baya daga gwamnatocin baya tun daga 2012.

“Na daidaita sama da Naira biliyan biyar na fansho da garatuti a cikin shekara daya a ofis kuma zan tabbatar da cewa duk wani ma’aikacin gwamnati da ya yi ritaya ya samu alawus-alawus dinsa da na fansho,” in ji shi.

Da yake karin haske, Lawal ya kara jaddada cewa gwamnatin sa na aiki ba dare ba rana domin ceto jihar ta fuskar zamantakewa da tattalin arziki.

“Bangarorin tsaro, ilimi, karfafa matasa, noma, kiwon lafiya, da shugabanci na gari za su ci gaba da samun karbuwa sosai a wani bangare na aikin ceton gwamnatina,” in ji shi.

Gwamnan ya yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da kasancewa masu bin doka da oda tare da marawa kyawawan manufofi da tsare-tsare na gwamnatin sa domin cimma burinta.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp