fidelitybank

Mun fara rasa wurin da zamu ajiye ‘yan Boko Haram a Borno – Hukumomi

Date:

Hukumomi a Jihar Borno, sun ce sun fara rasa wuraren da za su ajiye mayaƙan Boko Haram da suka miƙa wuya.

Babban jami’in soja Manjo Janar Chris Musa ya ce a yayin da miƙa wuyan da mayaƙan Boko Haram ɗin ke yi yake taimakawa wajen shawo kan rikicin da ya addabi yankin, a gefe guda kuma babu isassun wuraren ajiye su.

Babban janar ɗin ya ce zuwa yanzu akwai mayaƙan da suka yi saranda kuma suke jiran bin matakan sauya musu tunani, amma ba su da wajen ajiye su.

Wuraren ajiye mutanen sun cika maƙil – kuma a yanzu hukumomi suna duba yiwuwar gina wasu.

Matakan sauyawa da gyara tunani na cikin ƙoƙarin da gwamnatin Najeriya ke yi don kawo ƙarshen ayyukan masu iƙirarin jihadi, musamman a arewa maso gabashin ƙasar. In ji BBC.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta yi ƙiyasin cewa kusan mutum 350,000 ne suka mutu a rikici tsakanin ƙungiyar Boko Haram da rundunar sojin ƙasar cikin shekara 12. Amma adadin ka iya fin haka.

Janar Chris Musa ya ce, wani babban ƙalubalen shi ne yadda suke samun matsalar mayar da ƴan gudun hijira matsugunansu.

Hakan na faruwa ne sakamakon ƴan tayar da ƙayar bayan sun daddasa nakiyoyi a kan hanya.

nasarawa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp