fidelitybank

Mun fara haƙo ɗanyen mai ganga miliyan ɗaya da dubu ɗari takwas a rana – NNPCL

Date:

Kamfanin mai na kasa NNPCL ya ce, ya samu nasarar kai ga haƙo ɗanyen mai ganga miliyan ɗaya da dubu ɗari takwas a kowacce rana.

Shugaban Kamfanin Malam Mele Kyari ne ya bayyana hakan a yau Alhamis, yayin taron manema labarai da ya gudana a Abuja.

Ya ce alƙaluman da aka samu sun haɗa daga watan Yuni zuwa Nuwamban da muke ciki.

Kamfanin wanda cikin shekaru 15 da suka gabata ya yi ta fama da rashin taron na masu ruwa da tsaki, ya mayar da hankali ne kan harkokin kasuwancin masu zuba jari kuma hakan ya ja raguwar yawan gangar man da yake samarwa a kowacce rana.

Malam Mele ya ce suna ta fafutukar ganin yadda za su haɓaka yawan man da ake haƙowa domin ci gaban ƙasar da kuma saukakawa al’umma.

“An taɓa haƙo ganga miliyan biyu da dubu ɗari biyar a sehkarun baya, amma daga nan aka yi ta fama da rashin saka jari da kuma rashin tsaro har ta kai man da kae haƙo wa ya yi ƙasa zuwa ganga miliyan ɗaya da dubu ɗari huɗu a wannan shekara,” in ji shi.

Ya ce hakan ne ya sa suka tashi da yin aiki tukuru don samo bakin zaren matsalar.

“Amma zuwa watan Yuni mun ka zuwa ganga miliyan ɗaya da dubu ɗari takwas,” in ji Kyari.

Ya ce nasarar za ta sa a samu ƙarin arziki a ƙasar da haraji da sauransu.

“A iya sanina babu dogayen layukan mai ba a Najeriya. Cire tallafi ne ya janyo aka samu sauki,” in ji shugaban na NNPCL.

A ɗaya gefen, Malam Lawal Musa babban mai ba da shawara kan kasuwancin NNPCL, ya ce an samu ƙaruwar yawan gas ɗin da ake haƙowa a kasar.

NNPCL ya ce cikin shekaru biyu da suka gabata, ya cire haramtattun bututan layin mai daga jikin nasa da ya kai 5,800.

legitnewsnigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp