fidelitybank

Mun fara binciken wasan da aka bayar da jan kati 15 – FIFA

Date:

Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA na gudanar da bincike a kan kasashen Argentina da Netherlands, bayan wasan daf da na kusa da karshe na gasar cin kofin duniya da aka yi ranar Juma’a.

Zakarun Kudancin Amurka, Argentina ta yi nasara da ci 4-3 a bugun fenareti a filin wasa na Lusail, bayan da tun farko ta yi rashin nasara da ci biyu da nema, inda wasan ya tafi nesa.

Alkalin wasa Antonio Mateu Lahoz ya ba da katunan 15 ga ‘yan wasan da suka taka rawa a wasan mafi yawa a tarihin gasar cin kofin duniya, inda suka wuce Kamaru da Jamus a 2002 (14).

An kuma bai wa dan wasan baya na Netherlands Denzel Dumfries jan kati bayan kammala wasan.

An tashi wasan ne a minti na 89 a lokacin da Leandro Paredes ya yi wa Nathan Ake keta sannan ya buga kwallon a ragar Netherlands.

Dukkanin ‘yan wasa da ma’aikatan kociyan sun yi karo da juna, duk da cewa tashin hankali ya sake yin barazanar barkewa a cikin karin lokaci da kuma a bugun daga kai sai mai tsaron gida.

A wata sanarwa da FIFA ta fitar a ranar Asabar,  ta ce, an bude shari’a kan hukumar kwallon kafa ta Argentina da kuma hukumar kwallon Holland.

Laifin ya shafi yiwuwar keta doka ta 12 na kundin ladabtarwa na FIFA da rashin da’a na ‘yan wasa da jami’ai.

Ana kuma binciken bangaren Lionel Scaloni kan wani karin yuwuwar keta doka ta 16, wanda ya shafi tsari da tsaro a wasannin.

asuu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp