Rundunar ‘yan sandan jihar Osun, ta tabbatar da wani faifan bidiyo da ke yawo na wani jami’in ‘yan sandan da ya ce babban jami’inta ya ci zarafinta.
Insifeto Olorunsogo Bamidele a wani faifan bidiyo da ya fara yaduwa a kafafen sada zumunta na zamani ya yi zargin cewa jami’in da ke kula da laifuka (DCO) reshen ‘yan sanda na Ode-Omu, ASP Ajayi Matthew ya kai mata hari.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan, Yemisi Opalola ya sanya wa hannu, ya ce kwamishinan ‘yan sandan, Faleye Sunday Olaleye na sane da bidiyon.
Sanarwar ta bayyana cewa, CP din ya yi hira da bangarorin da abin ya shafa, sannan ya kuma ba da umarnin gudanar da bincike mai zurfi don bankado al’amuran da suka haifar da munanan dabi’u.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Kwamishanan ‘yan sandan jihar Osun, CP Faleye S. Olaleye, na son sanar da jama’a cewa rundunar ta na sane da faifan bidiyon wata mata sifeton ‘yan sanda, Olorunsogo Bamidele da ake zargin DCO, ASP Ajayi Mathew, ya ci zarafinta. Ode Omu division trending on social media.
“CP a cikin gaggawar shiga tsakani ya yi hira da Jami’an ‘yan sanda (jam’iyyun) da ke da hannu a cikin wannan aikin na rashin da’a kuma saboda haka ya ba da umarnin yin bincike game da lamarin don gano yanayin da ya haifar da wannan mummunar dabi’a.”
Rundunar ‘yan sandan ta tabbatar wa jama’a cewa za a yi adalci a kan lamarin.