fidelitybank

Mun fara bincike akan Askarawan mu da ake zargi da wuce gona da iri – Zamfara

Date:

Gwamnatin jihar Zamfara ta ce, tana gudanar da bincike kan zargin da ake yi wa Askarawan jihar cewa, suna wuce gona da iri wajen gudanar da ayyukansu na tabbatar da tsaro a yankunan jihar.

Wannan na zuwa ne bayan zargin da wasu mazauna Tsafe suka yi cewa, Askarawan sun kama tare da kashe musu ‘yan uwa a lokacin da suke tsare da su.

Ƴan uwan waɗanda abin ya shafa sun zargi Askarawan da ke aiki a karamar hukumar Tsafe da kashe wani matashi mai suna Hamza bayan kama shi.

“Wani kaninmu ya tafi gona nan Tsafe, dama bisashe na masa É“arna kullum yana can yana tsare gonar tasa. Ranar sai ya faÉ—a wa mai bisashen cewa idan suka sake masa É“arna zai kai su ga huÆ™uma,” in ji É—an uwan mamacin.

Ya ce matan da ya kai karar wurinsu a ce matan ƴan askarawan ne, inda matan suka kira mazajensu suka ce matashin na musu ɓarazana.

“Daga nan ne suka zo suka kama shi su ka je da shi ofis É—in su suka riÆ™a dukansa, jini yana fita ta kunnesa,” in ji É—an uwan.

Wannan dai ba shi ne karon farko da ake samun faruwar irin haka da ya shafi askarawa a yankin Tsafe ba, inda ko a kwanan baya an samu wani al’amari da ya shafi wani magidanci da ake zargin ya rasa ransa lokacin da yake tsare a hannun askarawan.

Mazauna yankin sun buƙaci hukumomin Zamfara da su yi wa mamatan adalci ta hanyar ɗaukar mataki akan waɗanda ake zargi ta hanyar hukunta su idan aka same su da laifi.

Sai dai gwamnatin jihar ta Zamfara ta shaida wa BBC cewa ba ta da matsaniya kan al’amarin, amma a shirye take domin gudanar da bincike.

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maÆ™iya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...
X whatsapp