Gwamnatin jihar Zamfara ta ce, tana gudanar da bincike kan zargin da ake yi wa Askarawan jihar cewa, suna wuce gona da iri wajen gudanar da ayyukansu na tabbatar da tsaro a yankunan jihar.
Wannan na zuwa ne bayan zargin da wasu mazauna Tsafe suka yi cewa, Askarawan sun kama tare da kashe musu ‘yan uwa a lokacin da suke tsare da su.
Ƴan uwan waɗanda abin ya shafa sun zargi Askarawan da ke aiki a karamar hukumar Tsafe da kashe wani matashi mai suna Hamza bayan kama shi.
“Wani kaninmu ya tafi gona nan Tsafe, dama bisashe na masa É“arna kullum yana can yana tsare gonar tasa. Ranar sai ya faÉ—a wa mai bisashen cewa idan suka sake masa É“arna zai kai su ga huÆ™uma,” in ji É—an uwan mamacin.
Ya ce matan da ya kai karar wurinsu a ce matan ƴan askarawan ne, inda matan suka kira mazajensu suka ce matashin na musu ɓarazana.
“Daga nan ne suka zo suka kama shi su ka je da shi ofis É—in su suka riÆ™a dukansa, jini yana fita ta kunnesa,” in ji É—an uwan.
Wannan dai ba shi ne karon farko da ake samun faruwar irin haka da ya shafi askarawa a yankin Tsafe ba, inda ko a kwanan baya an samu wani al’amari da ya shafi wani magidanci da ake zargin ya rasa ransa lokacin da yake tsare a hannun askarawan.
Mazauna yankin sun buƙaci hukumomin Zamfara da su yi wa mamatan adalci ta hanyar ɗaukar mataki akan waɗanda ake zargi ta hanyar hukunta su idan aka same su da laifi.
Sai dai gwamnatin jihar ta Zamfara ta shaida wa BBC cewa ba ta da matsaniya kan al’amarin, amma a shirye take domin gudanar da bincike.