fidelitybank

Mun fara bincike a kan kashe mana Insifeta da Sojojin ruwa suka yi – ‘Yan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sanda a jihar Legas ta ce, ta fara gudanar da bincike kan zargin kashe wani sifeton ‘yan sanda da wasu jami’an sojin ruwa suka yi a yankin Okokomaiko da ke Ojo.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar wa NAN haka a ranar Lahadi.

Hundeyin ya ce an samu rahoton faruwar lamarin a ofishin ‘yan sanda na Okokomaiko da misalin karfe 4:30 na yammacin ranar Asabar daga wasu jama’a.

Ya ce rahoton ya nuna cewa wasu ‘yan sanda da ke sintiri na yau da kullum a kan yankin Igbo-Elerin, sun yi kokarin damke wani babur da ke kan hanya a tashar Beno.

Kakakin ya ce wasu mutane biyu da ke kan babur din, wadanda ke sanye da mufti, wadanda suka ce jami’an sojin ruwa ne, sun yi turjiya da kama su, suka far wa ‘yan sandan.

“Sauran jami’an sojan ruwa sanye da kakinsu sun isa wurin inda suka goyi bayan abokan aikinsu a harin.

“A lokacin da wani Sufeto ya fado ya sume, sai jami’an Sojin ruwa suka tsere daga wurin.

“An ceto sufeton kuma an garzaya da shi asibiti a yankin, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

“An ajiye gawar a dakin ajiye gawa na Idi-Araba, Yaba, domin a tantance gawarwakin, yayin da ake ci gaba da bincike,” in ji shi.

breaking news in nigeria today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp