Kwamishiniyar Ma’aikatar kula da Mata da Walwalar Kananan Yara ta jihar Kano, ta ce za ta fara gudanar da bincike a gidan Yara na Nasarawa, sakamakon korar wasu Yara goma sha daya da a ka yi a gidan, biyo bayan wani rikici da suka yi a tsakanin su.
Kwamishiniyar ma’aikatar Hajiya Aisha Lawan Saji, ta bayyana hakan a wani zagayen rangadi da ta kai gidan Yaran da aka ware musu.
Hajiya Aisha Saji, ta kuma bayyana godiyar ta ga masu kula da gidajen, musamman ganin yadda su ke baiwa yaran tarbiyar da ake bukata.
Ta kuma ce gwamnatin Kano za ta bijiro da hanyar yin aure a tsakanin Yaran da suka girma domin aurer da su a tsakanin juna.
Ta kara da cewa a shirye ma’aikatar ta take, domin bayar da dukannin gudunmawa, don kula da Yaran.