fidelitybank

Mun damu kwarai a kan ‘yan siyasan da su ke siyan katin zabe – INEC

Date:

Gabanin zaben 2023 mai gabatowa, Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta koka da yadda a yanzu ‘yan siyasa ke sayen katin zabe na dindindin, PVC, domin yin magudi tare da bata sahihancin aikin.

Wannan bayanin na zuwa ne a daidai lokacin da masu kada kuri’a a fadin kananan hukumomi 774 da ke fadin kasar nan suka fito domin karbar katin zabe. Wannan tsari ya fara ne a ranar 12 ga Disamba kuma ana sa ran zai ƙare a ranar 27 ga Janairu 2023.

Mukaddashin shugaban hukumar zabe ta INEC kuma kwamishinan kasa mai kula da babban birnin tarayya Abuja, Nasarawa, Kaduna da Filato Mohammed Haruna ne ya bayyana hakan a ranar Litinin yayin kaddamar da shirin #VoteMatters na wata kungiyar sa ido kan zabe mai suna NESSACTION a Abuja.

Haruna ya bayyana cewa, a kwanakin baya ne Hukumar ta kama wasu mutane biyu a jihohin Sokoto da Kano bisa laifin mallakar PVC ba bisa ka’ida ba.

Ya kuma jaddada cewa a yanzu ‘yan siyasa suna sayen katin zabe, inda ya gargadi masu kada kuri’a da kada su sayar da katinsu saboda kowane dalili, saboda laifi ne da za a hukunta su.

Ya ce, “Wasu daga cikin ku na sane da cewa a baya-bayan nan ne INEC ta yi nasarar hukunta wasu mutane biyu da aka samu da laifin mallakar PVC ba bisa ka’ida ba a Kano da Sakkwato. Don haka ina kira ga jama’a da su tattara PVCs din su, su kiyaye su, sannan su tabbatar kun fita can ku kada kuri’u a ranar zabe domin ba za ku iya kada kuri’a ba tare da PVC din ku ba.”

nnn-news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp