fidelitybank

Mun damke manomin tabar wiwi irin ta Indiya a Sokoto – NDLEA

Date:

Hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa NDLEA, ta ce jami’anta sun kama wani da ake zargin manomin tabar wiwi irin ta kasar Indiya a jihar Sokoto.

Kwamandan hukumar ta NDLEA a jihar, Mista Adamu Iro, ya shaida wa manema labarai ranar Asabar cewa “Wannan shi ne karo na farko da aka samu irin wannan lamari a tarihin jihar”.

A cewar Iro, wanda ake zargin, Anas Sani, an kama shi ne a kauyen Sayinna da ke karamar hukumar Tambuwal, bayan da aka samu labari.

Ya ce wanda ake zargin ya shuka nau’in tabar wiwi na kasar waje a cikin gonarsa ta masara, wadda jami’an NDLEA suka tayar da su suka mamaye gonar.

Kwamandan ya kara da cewa za a gurfanar da wanda ake zargin bayan binciken dakin gwaje-gwaje na ganyen da aka tumbuke.

Ya godewa mazauna yankin bisa goyon bayan da suke baiwa hukumar, ya kuma bukace su da kada su yi kasa a gwiwa, yana mai gargadin cewa noman hemp na Indiya da mu’amala da miyagun kwayoyi na jawo hukunci mai tsanani.

vangurd 
news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp