Ministan harkokin sadarwa da fasahar zamani, Isa Ali Pantami, ya ce, sau 66 suke daƙile yunƙurin kutse daga Turai, domin ganin yadda majalisar zartarwar tarayyar Najeriya ke tattaunawa ta intanet.
Yace duka kutsen da aka yi ƙoƙarin yi, an kai rahotansu ga hukumomin da suka dace a kan lokacin kuma aka ɗauki matakin da ya dace.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da ake taron bitar gwamnatin Shugaba Buhari daga (2015-20230) karo na 19.
Yace an gabatar da tattaunawar majalisar zartarwar sau 108 tun daga watan Oktoban 2020, domin gudanar da ayyuka da tarukan gwamnati ta intanet.
Yace da an gudanar da waɗan nan taruka a fili da Njeriya ta kashe naira biliyan 47.