fidelitybank

Mun dakile harin ‘yan ta’addan da suka kaiwa gwamnan Yobe hari – Sojoji

Date:

Hedikwatar tsaro ta tabbatar da cewa dakarun runduna ta 29 Task Force Brigade, sun dakile wani hari da wasu ‘yan ta’adda suka kai wa ayarin motocin Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni a hanyar Maiduguri zuwa Damaturu ranar Asabar.

Wata sanarwa da Daraktan Ayyuka na Yada Labarai na Tsaro, Maj.-Gen. Edward Buba, a ranar Litinin a Abuja, ya ce sojojin sun kuma kwato motoci biyu da lamarin ya shafa.

Ya ce direban babbar motar soji daya, ‘yan sanda hudu da jami’an DSS daya da suka samu raunuka a harin na cikin koshin lafiya.

A cewarsa, daya daga cikin ‘yan sandan da suka rakata ya mutu ne jim kadan da isar su asibitin kwararru na Damaturu.

“Rundunar sojojin ta 29 Task Force Brigade karkashin jagorancin kwamandan birgediya suna gudanar da sintiri na yaki a yankin domin gano ‘yan ta’addan da suka aikata wannan aika aika.

“Motoci biyu da lamarin ya shafa sun hada da, MRAP na soji daya da kuma wata motar rakiyar farar hula daya da aka harba tayoyinsu a lokacin da lamarin ya faru, an kwato su cikin koshin lafiya zuwa sansanin sojoji da ke Benisheikh.

“Ana ci gaba da gudanar da ayyukan farauta tare da lalata ‘yan ta’addar da suka kai harin,” in ji shi.

Kamfanin dillancin labarai na Najeriya (NAN) ya tuna cewa ‘yan ta’adda sun yi wa ayarin motocin gwamnan kwanton bauna a lokacin da suke komawa Damaturu daga Maiduguri, kimanin kilomita 6 daga garin Benesheikh a ranar Asabar.

Gwamnan ba ya cikin ayarin motocin a lokacin da aka yi musu kwanton bauna.

Sakataren gwamnatin jihar da wasu manyan jami’an gwamnatin da ke cikin ayarin ba su ji rauni ba.

naija news legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp