Gwamnan Bauchi Bala Mohammed ya amince a bayar da tallafin rabin kuɗin da hukumar aikin hajji ta ƙara wa maniiyatan bana, ma’ana gwanatinsa za ta biya kashi 50 na ƙarin.
Cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a, Gwamnan ya ce idan aka yi la’akari da matsalar tattalin arzikin da ake ciki a Najeriya, ya amince da abiya rabin kuɗin da aka ƙara musu da za su biya.
“Na biya naira 950,000 ga duk wani maniyyaci da ya fito daga jihar Bauchi, kenan kashi 50 na kuɗin. Na kuma bai wa hukumar umarnin ta mayarwa da waɗanda suka riga suka biya nasu adadin abin da na biya musu, kuma a cikawa wadanda ba su da shi nan da lokacin da wa’adi zai cika.” in ji Gwamnan.
A makon jiya ne hukumar alhazai ta Najeriya ta sanar da ƙarin kudin aikin hajji ga maniyyatan ba da naira miliyan 1,918,032, ga waɗanda aka riga aka karbi kudadensu, wanda kuma zai biya daga baya sai ya biya sama da naira miliyan takwas.