fidelitybank

Mun ceto Matashin da ya so rataye kansa a kan bashi a Kano – ‘Yan Kwana-Kwana

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ta yi nasarar kubutar da wani mutum mai shekaru 37 da ke daf da kashe kansa ta hanyar rataye kansa a kan bishiya.

Mutumin mai suna Saifullah Rabi’u ya ajiye takardar kashe kansa ne da ke nuni da cewa ya yanke kauna ne ya sa ya ci bashin Naira miliyan 2 da ake bin sa wajen neman bizar kasar waje.

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.

A cewar sanarwar, babban dakin kula da hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa da misalin karfe 10:07 na safe daga ma’aikatar ayyuka da gidaje ta jihar Kano, inda suka kai rahoton faruwar lamarin a hanyar jihar ta gidan Sarkin Nasarawa.

Da aka samu wannan kiran, jami’an kashe gobara da ke bakin aiki sun tattaru zuwa wurin, inda suka isa da misalin karfe 10:10 na safe.

Ya ce sun samu Saifullahi Rabiu a cikin wani hali na rashin lafiya, yana kokarin kashe kansa ta hanyar rataye a jikin bishiya.

A cikin takardar kashe kansa, Rabi’u ya bayyana dimbin bashin da ake binsa, inda ya bayyana cewa tuni ya mayar da kusan Naira 500,000 na kudaden da ya karbo.

Ya koka da cewa kalubale da abin kunya daga mai karbar bashi ya sa shi ya yi tunanin kashe kansa.

Abdullahi ya bayyana cewa an mika mutumin da aka ceto Saifullah Rabiu ga jami’in kula da laifuka (D.C.O) Zaharaddini na sashin ‘yan sanda na Farm Center domin ci gaba da bincike.

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp