fidelitybank

Mun ceto Matashin da ya so rataye kansa a kan bashi a Kano – ‘Yan Kwana-Kwana

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kano, ta yi nasarar kubutar da wani mutum mai shekaru 37 da ke daf da kashe kansa ta hanyar rataye kansa a kan bishiya.

Mutumin mai suna Saifullah Rabi’u ya ajiye takardar kashe kansa ne da ke nuni da cewa ya yanke kauna ne ya sa ya ci bashin Naira miliyan 2 da ake bin sa wajen neman bizar kasar waje.

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano Saminu Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya rabawa manema labarai.

A cewar sanarwar, babban dakin kula da hukumar kashe gobara ta samu kiran gaggawa da misalin karfe 10:07 na safe daga ma’aikatar ayyuka da gidaje ta jihar Kano, inda suka kai rahoton faruwar lamarin a hanyar jihar ta gidan Sarkin Nasarawa.

Da aka samu wannan kiran, jami’an kashe gobara da ke bakin aiki sun tattaru zuwa wurin, inda suka isa da misalin karfe 10:10 na safe.

Ya ce sun samu Saifullahi Rabiu a cikin wani hali na rashin lafiya, yana kokarin kashe kansa ta hanyar rataye a jikin bishiya.

A cikin takardar kashe kansa, Rabi’u ya bayyana dimbin bashin da ake binsa, inda ya bayyana cewa tuni ya mayar da kusan Naira 500,000 na kudaden da ya karbo.

Ya koka da cewa kalubale da abin kunya daga mai karbar bashi ya sa shi ya yi tunanin kashe kansa.

Abdullahi ya bayyana cewa an mika mutumin da aka ceto Saifullah Rabiu ga jami’in kula da laifuka (D.C.O) Zaharaddini na sashin ‘yan sanda na Farm Center domin ci gaba da bincike.

today nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp