Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta bayyana cewa, jami’anta da hadin gwiwar ‘yan banga sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda a kauyen Kadamutsa da ke karamar hukumar Zurmi a jihar tare da ceto mata 6 da wani yaro dan shekara daya.
Wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Mohammed Shehu ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Gusau, ta ce jami’an ‘yan sanda da ’yan banga sun yi aiki da bayanan da suka shafi sace mata shida da yaron.
“Jami’an ‘yan sanda sun tattaru zuwa wurin da aka gudanar da aikin bincike da ceto tare da yankin Zurmi – Jibiya, wanda ya kai ga ceto duk wadanda abin ya shafa ba tare da wani sharadi ba,” in ji shi.
“An kai wadanda lamarin ya rutsa da su asibiti domin a duba lafiyarsu, jami’an ‘yan sanda sun bayyana su tare da mika iyalansu.”
Shehu ya ce kwamishinan ‘yan sanda, Mista Kolo Yusuf ya yabawa jami’an ‘yan sanda da ’yan banga bisa nasarar da suka yi na ceto su, ya kuma taya wadanda abin ya shafa murnar samun ’yanci.
A cewar sanarwar, kwamishinan ya sake nanata kudurin rundunar na ci gaba da kawar da jihar daga aikata miyagun laifuka tare da kama masu aikata munanan laifuka a fadin jihar.
Daga nan sai Kwamishinan ya yi kira ga jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro da muhimman bayanai da za su iya samar da zaman lafiya mai dorewa a Jihar.