fidelitybank

Mun ceto mata 6 da yaro ɗaya a Zamfara – Ƴan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara ta bayyana cewa, jami’anta da hadin gwiwar ‘yan banga sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda a kauyen Kadamutsa da ke karamar hukumar Zurmi a jihar tare da ceto mata 6 da wani yaro dan shekara daya.

Wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Mohammed Shehu ya sanya wa hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Gusau, ta ce jami’an ‘yan sanda da ’yan banga sun yi aiki da bayanan da suka shafi sace mata shida da yaron.

“Jami’an ‘yan sanda sun tattaru zuwa wurin da aka gudanar da aikin bincike da ceto tare da yankin Zurmi – Jibiya, wanda ya kai ga ceto duk wadanda abin ya shafa ba tare da wani sharadi ba,” in ji shi.

“An kai wadanda lamarin ya rutsa da su asibiti domin a duba lafiyarsu, jami’an ‘yan sanda sun bayyana su tare da mika iyalansu.”

Shehu ya ce kwamishinan ‘yan sanda, Mista Kolo Yusuf ya yabawa jami’an ‘yan sanda da ’yan banga bisa nasarar da suka yi na ceto su, ya kuma taya wadanda abin ya shafa murnar samun ’yanci.

A cewar sanarwar, kwamishinan ya sake nanata kudurin rundunar na ci gaba da kawar da jihar daga aikata miyagun laifuka tare da kama masu aikata munanan laifuka a fadin jihar.

Daga nan sai Kwamishinan ya yi kira ga jama’a da su taimaka wa jami’an tsaro da muhimman bayanai da za su iya samar da zaman lafiya mai dorewa a Jihar.

nhgsfp

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Peter Obi na nan a cikin jam’iyyar har yanzu – LP

Shugaban ƙungiyar Obidient Movement, Dr. Tanko Yunusa ya ce...

Yadda Mahara sun kashe mutum biyu, sun ƙona gidaje a Filato

Wasu da ake zargin mahara sun afka wa karamar...

An YI zanga-zanga a Isra’ila kan shirin Netanyahu na mamaye Gaza

Dubban mutane sun fito kan tituna a faɗin Isra'ila,...

Birtaniya za ta fara tisa ƙeyar bakin da suka aikata laifi zuwa kasarsu

Birtaniya ta fitar da sabon tsarin tisa keyar duk...

NDLEA ta kama Fasto kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Gwamnoni sun mika sakon ta’azziya ga iyalan Audu Ogbeh

Shugaban ƙungiyar gwamnonin arewa kuma gwamnan jihar Gombe, Muhammadu...

Duk wahala sai dai mu mutu a Gaza – Fatma

Wata mai mai ƴaƴa tara ta ce, duk runtsi...

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...
X whatsapp