Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin ranar jimami a jihar, inda ya amince da ba ma’aikatan jihar hutun aiki domin alhinin waɗanda suka rasu daga cikin tawagar ƴanwasanta da suke yi hatsari a hanyarsu ta komawa gida daga wasannin ƙasa da aka yi a Ogun.
Zuwa yanzu dai inda mutum 22 suka rasu daga cikin tawagar ƴanwasan, sannan wasu kuma suka jikkata.
A sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce gwamnan ya kaɗu matuƙa da samun labarin mutuwar ƴanwasan, lamarin da ya bayyana da yanayi mai ɗaga hankali da damuwa.
“A madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano, muna miƙa ta’aziyarmu ga iyaye da iyali da ƴanuwan waɗanda suka rasu. Sanan ina kira ga dukkan musulmi a jihar da su yi addu’ar samun rahamar Allah ga waɗanda suka rasu.”
Gwamnan ya kuma ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa wajen kula da waɗanda suka jikkata, da kuma tallafa wa iyalan waɗanda suka rasu.