fidelitybank

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Date:

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar Litinin ranar jimami a jihar, inda ya amince da ba ma’aikatan jihar hutun aiki domin alhinin waɗanda suka rasu daga cikin tawagar ƴanwasanta da suke yi hatsari a hanyarsu ta komawa gida daga wasannin ƙasa da aka yi a Ogun.

Zuwa yanzu dai inda mutum 22 suka rasu daga cikin tawagar ƴanwasan, sannan wasu kuma suka jikkata.

A sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ya ce gwamnan ya kaɗu matuƙa da samun labarin mutuwar ƴanwasan, lamarin da ya bayyana da yanayi mai ɗaga hankali da damuwa.

“A madadin gwamnati da al’ummar jihar Kano, muna miƙa ta’aziyarmu ga iyaye da iyali da ƴanuwan waɗanda suka rasu. Sanan ina kira ga dukkan musulmi a jihar da su yi addu’ar samun rahamar Allah ga waɗanda suka rasu.”

Gwamnan ya kuma ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa wajen kula da waɗanda suka jikkata, da kuma tallafa wa iyalan waɗanda suka rasu.

legit.ng.news.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp