fidelitybank

Mun baiwa Ɗalibai bashin kuɗi na biliyan 2.1 a yankin Kudu maso Gabas – Asusun bayar da lamuni

Date:

Asusun ba da lamuni na ilimi na ƙasar nan, NELFUND, ya amince da bayar da lamuni ga dalibai ga manyan makarantu biyar a yankin Kudu maso Gabas da wasu yankuna 35 na kasar nan.

NELFUND ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma’a, inda ta bayyana kashi na biyu na raba kudaden.

Makarantun Kudu-maso-Gabas sun hada da Federal Polytechnic, Nekede, Jihar Imo; Jami’ar Jihar Ebonyi; Jami’ar Jihar Abia; Michael Okpara University of Agriculture, Umudike; da Alex Ekwueme Federal University, Anambra State.

Hukumar ta kuma bayyana cewa, an raba jimillar Naira biliyan 2.1 ga wasu karin manyan makarantu 40, wanda ya kai adadin cibiyoyin da suka ci gajiyar tallafin zuwa 59.

Ma’anar ita ce, daliban Najeriya da ke cibiyoyi a fadin kasar sun ci gajiyar shirin ba da lamuni na dalibai, wanda aka kashe Naira biliyan 50 a kasafin kudin shekarar 2024.

NELFUND ta kara da cewa, “Wannan fadada wani muhimmin ci gaba ne a ci gaba da kokarin NELFUND na samar da damar samun ingantaccen ilimi ga dukkan daliban Najeriya, ba tare da la’akari da yanayin kudinsu ba.”

Biyan kudin na baya-bayan nan ya zo ne watanni bayan da NELFUND ta fitar da Naira biliyan 1.17 a matsayin kudaden hukumomin, wanda ya kunshi mutane 20,000 da suka ci gajiyar shirin.

Sai dai kungiyar koli ta al’adun kabilar Igbo, Ohanaeze Ndigbo Youth Council Worldwide, ta nuna fushinta a baya dangane da ware cibiyoyin daga yankin Kudu maso Gabas a matakin farko na shirin bayar da lamuni na dalibai.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp