Ƙungiyar Malaman Jami’a ta ASUU, ta bai wa gwamnatin tarayya wa’adin mako biyu cewa za su tafi yajin aiki idan har ba a biya musu buƙatunsu ba.
Wannan dai na zuwa ne bayan ƙarewar wa’adin kwana 21 da ƙungiyar ta bayar a baya.
ASUU dai na son ganin an kammala zartar da batutuwan da ke cikin yarjejeniyar da ta cimma da gwamnatin tarayya ta 2009 da kuma biyan ƴaƴan ƙungiyar albashinsu na watanni takwas da aka riƙe musu saboda yajin aikin da ƙungiyar ta yi na kusan shekara guda.
Harwayau ƙungiyar ta ASUU na son ganin gwamnati ta inganta jami’o’in ƙasar da kuma biyan su alawus-alawus da aka sanya wani ɓangarensa a kasafin kuɗin shekarar 2023.
Sauran batutuwan sun haɗa damuwa da irin yadda ake samun ƙaruwar jami’o’i da batun tsarin biyan su albashi.