fidelitybank

Mun baiwa gwamnati wa’adi ta gaggauta ceto Ɗaliban koyon aikin likita 20 da aka sace – NANS

Date:

Ƙungiyar ɗaliban Najeriya (NANS), ta ba gwamnati wa’adin mako biyu ta ceto ɗaliban koyan aikin likita 20 da ƴan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Benue.

Ɗaliban da suka ƙunshi ƴan jihar Borno, da jihar Filato, na kan hanyarsu ne ta zuwa jihar Ogun domin halartar wani taro.

Muhammad Sabo, wanda shi ne mataimakin shugaban ƙungiyar ɗaliban Najeriyar, ya shaida wa BBC cewa “An yi irin wannan abu ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba, shi ya sa a wannan karo ba za mu bayar da ƙofa yadda za a cutar da ɗalibanmu ba.”

Ya bayyana cewa shi ya sa ƙungiyar ta ɗeba wa gwamnati wa’adi domin ganin ta yi duk abin da ya kamata domin kuɓutar da ɗaliban.

Ya ƙara da cewa “saɓanin hakan zai sa a ga fushinmu fiye da yadda aka saba gani.”

Ya kuma nuna takaici kan yadda makarantun Najeriya da dama ke fama da matsalar tsaro, wanda hakan ya sanya aka rufe wasu makarantun da dama.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp