fidelitybank

Mun baiwa gwamnati wa’adi ta gaggauta ceto Ɗaliban koyon aikin likita 20 da aka sace – NANS

Date:

Ƙungiyar ɗaliban Najeriya (NANS), ta ba gwamnati wa’adin mako biyu ta ceto ɗaliban koyan aikin likita 20 da ƴan bindiga suka yi garkuwa da su a jihar Benue.

Ɗaliban da suka ƙunshi ƴan jihar Borno, da jihar Filato, na kan hanyarsu ne ta zuwa jihar Ogun domin halartar wani taro.

Muhammad Sabo, wanda shi ne mataimakin shugaban ƙungiyar ɗaliban Najeriyar, ya shaida wa BBC cewa “An yi irin wannan abu ba sau ɗaya ba ba sau biyu ba, shi ya sa a wannan karo ba za mu bayar da ƙofa yadda za a cutar da ɗalibanmu ba.”

Ya bayyana cewa shi ya sa ƙungiyar ta ɗeba wa gwamnati wa’adi domin ganin ta yi duk abin da ya kamata domin kuɓutar da ɗaliban.

Ya ƙara da cewa “saɓanin hakan zai sa a ga fushinmu fiye da yadda aka saba gani.”

Ya kuma nuna takaici kan yadda makarantun Najeriya da dama ke fama da matsalar tsaro, wanda hakan ya sanya aka rufe wasu makarantun da dama.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...
X whatsapp