Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya ce ya bai wa matatar mai ta Dangote gangar ɗanyen mai miliyan 30, sannan kuma kamfanin na shirin ƙara wa matatar ganga miliyan 17 cikin wata biyu.
Mataimakin shugaban Kamfanin NNPCL, mai kula da fannin sayar da mai, Adedapo Segun, ne ya bayyana haka ranar Alhamis lokacin da yake zantawa da gidan talbijin na Arise Tv a ƙasar.
Mista Segun ya ce kamfanin zai samar wa matatar ganga miliyan 6.3 cikin watan Satumban da muke ciki, da kuma ƙarin ganga miliyan 11.3 cikin watan Oktoba mai zuwa.
Ya ƙara da cewa matakin na cikin ƙudurin gwamnatin tarayya na sayar wa matatun cikin ciki ɗanyen mai.
Mataimakin shugaban kamfanin man ya kuma kare matakin matsayin NNPCL na kasancewa shi kaɗai ke shigar da mai ƙasar da cewa kamfanin bai yi hakan da gayya ba, sai don yadda yanayin da kasuwar man ke ciki.