Shugaban tsare-tsare na masarautar Kano, Isah Bayero, ya baiwa jirgin Air Peace sa’o’i 72, su baiwa mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, hakuri bisa wulakantashi da suka yi da jinkirta tafiyarsa.
Isah Bayero ya bayyana hakan ranar Asabar yayin hira da wasu manema labarai a jihar Kano, rahoton Premium Times.
Ya ce, wajibi ne kamfanin Air Peace ya amsa cewa, ya yi laifi wajen kin bin tsari, wanda haka ya sabbaba jinkirin Sarkin Kano a tashar jirgin Legas.
Ya kuma ce: “Tunda mun yi jinkirin barin Banjul da awa guda, ya kamata su sani da akwai fasinjoji goma dake niyyar zuwa Kano, kuma suyi abinda ya kamata, saboda ba laifinmu bane jinkirin da ya faru.” In ji Isa Pilot.