Jam’iyyar PDP ta kara wa’adin sayar da fom din tsayawa takara da kuma mika fom din tsayawa takara a zaben 2023 mai zuwa.
Hakan ya fito ne cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ya fitar a daren Juma’a.
Sanarwar ta kara da cewa “Jam’iyyar PDP ta daidaita jadawalin ayyukanta don tsawaita kwanakin rufe saye da gabatar da fom na nuna sha’awa da tsayawa takara a babban zaben 2023,” in ji sanarwar.
An kara wa’adin ne domin a cike hutun kwana biyu da gwamnatin tarayya ta ayyana na bukukuwan Ista.