fidelitybank

Mulkin Obasanjo ya fi na Buhari da Tinubu da sauran su – El-Rufa’i

Date:

Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir el-Rufai, ya ce, wa’adi na biyu na tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo ne ya fi kowa nasara a fannin bunkasar tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya.

El-Rufai, tsohon gwamnan Kaduna ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin wani zama a taron Africa In the World a Stellenbosch, Afrika ta Kudu.

“Idan aka dubi yanayin tattalin arzikin Najeriya, shekaru hudu zuwa biyar mafi nasara na bunkasar tattalin arziki, samar da ayyukan yi, da rage hauhawar farashin kayayyaki shine lokacin wa’adin mulkin shugaba Obasanjo na biyu a shekarar 2003 zuwa 2007, inda a karon farko, kasar ta koma cikin ingantaccen tsarin hadaka kuma mun samu sa’a,” in ji shi.

A cewarsa, farashin man fetur ya fara hauhawa a wannan lokaci amma gwamnatin Obasanjo ba ta barnatar da iska ba.

El-Rufai ya ce lafiyar kasafin kudin Najeriya ta yi daidai a shekarar 2007, ta yadda lokacin da aka samu matsalar kudi a duniya a shekarar 2008, kasar ba ta ji haka ba.

“Babu wani abu da aka ji a Najeriya saboda Najeriya na da babban asusun ajiya,” in ji shi.

Ya kara da cewa a lokacin Najeriya tana da dimbin ajiyar kudi kuma gwamnati ta iya shawo kan lamarin ba tare da wata matsala ta cikin gida ba.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp