Mukaddashin firaministan Iraq, Mustapha al-Khadimi, ya yi kira da a kwantar hankula bayan magoya bayan malamin nan mai karfin fada aji a kasar Moqtada al-Sadr sun farma majalisar dokokin kasar karo na biyu a cikin mako guda.
Magoya bayan malamin da ke zaman dirshan a ginin majalisa da ke Bagadaza, na nuna adawarsu da zabin da aka yi wa wani mai goyon bayan Iran a matsayin dan takarar firaminista. A cewar BBC.
A jiya Asabar, an raunata mutane fiye da 120 a yayin zanga-zangar da aka yi a titunan birnin.
Wasu masu zanga zangar sun janye shingayen da aka sanya na kariya a wata gunduma mai suna Green Zone.
Hadakar jam’iyyar Mr Sadr ta samu rinjaye a mafi yawan kujerun majalisar a zaben da aka yi a watan Oktoban da ya wuce, to amma sun janye daga majalisar saboda kiki-kakar siyasa.