Shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado ya shigar da kara a gaban kotun masana’antu ta kasa da ke Abuja, ya na kalubalantar tsige shi da gwamnatin Ganduje ta yi a Kano.
A karar da Magaji ya shigar, gwamnatin jihar Kano ce tun a farko da ake tuhuma, yayin da aka saka sunayen manyan Lauyan jihar da majalisar dokokin jihar Kano da Akanta-Janar na jihar Kano da Barista Mahmud Balarabe da kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano a matsayin wadanda ake tuhuma na 2, 3, 4, 5 da 6, bi da bi.
Ya na rokon kotu da ta tantance ko ta duba da sashe na 8,15(i),(g), da (h), dokar hukumar korafe-korafen Jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008. Cikin 36 na (1) na kundin tsarin mulki kasa na shekara 1999.
Wanda ake kara na 1 zai iya sa wanda ake kara na 3 ya tantance koken wanda ake kara na hudu ta hanyar dakatar da wanda ake kara daga matsayinsa na shugaban hukumar kare kararrakin jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, neman hakkin mai da’awar na sauraron adalci.
Barista Muhuyi Magaji ta bakin lauyoyinsa, karkashin jagorancin Muhammad Ibrahim Tola, ya kuma bukaci kotun masana’antu ta kasa da ta tantance ko ta hanyar sashe na 4 (a), 5, da 6 na dokar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008.
Wanda ake kara na 5 ya na da hurumin ci gaba da gabatar da kansa a matsayin shugaban riko na Hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, bayan wa’adin watanni 1 ya dakatar da wanda ake tuhuma da wanda ake tuhuma na 1.
Ya roki kotun da ta bayar da sanarwar wanda ake kara na 3 ba shi da damar tantance koken wanda ake kara na 4 ta hanyar dakatar da wanda ake kara ba tare da ya fara jin ta bakin wanda ake kara ba ta hanyar da ya dace na kare kansa.
Idan za a iya tunawa majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da Barista Muhyi Magaji a matsayin shugaban hukumar tun a ranar 5 ga watan Yuli, bisa kin karbar jami’in mai mataki na 4 da aka tura ofishin sa, yayin da a ranar 26 ga wata ya ba da shawarar a kore shi, tare da gurfanar da shi, bisa zargin ya kawo takardar jabu ta rashin lafiya, sai dai kusan wata 7 da faruwar al’amarin har ya zuwa yau ba ace ufam ba, walau daga majalisa ko kuma gwamnatin Kano.