fidelitybank

Muhuyi ya shigar da kara ya na kalubantar tsige shi da gwamnati Kano ta yi

Date:

Shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado ya shigar da kara a gaban kotun masana’antu ta kasa da ke Abuja, ya na kalubalantar tsige shi da gwamnatin Ganduje ta yi a Kano.

A karar da Magaji ya shigar, gwamnatin jihar Kano ce tun a farko da ake tuhuma, yayin da aka saka sunayen manyan Lauyan jihar da majalisar dokokin jihar Kano da Akanta-Janar na jihar Kano da Barista Mahmud Balarabe da kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano a matsayin wadanda ake tuhuma na 2, 3, 4, 5 da 6, bi da bi.

Ya na rokon kotu da ta tantance ko ta duba da sashe na 8,15(i),(g), da (h), dokar hukumar korafe-korafen Jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008. Cikin 36 na (1) na kundin tsarin mulki kasa na shekara 1999.

Wanda ake kara na 1 zai iya sa wanda ake kara na 3 ya tantance koken wanda ake kara na hudu ta hanyar dakatar da wanda ake kara daga matsayinsa na shugaban hukumar kare kararrakin jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, neman hakkin mai da’awar na sauraron adalci.

Barista Muhuyi Magaji ta bakin lauyoyinsa, karkashin jagorancin Muhammad Ibrahim Tola, ya kuma bukaci kotun masana’antu ta kasa da ta tantance ko ta hanyar sashe na 4 (a), 5, da 6 na dokar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008.

Wanda ake kara na 5 ya na da hurumin ci gaba da gabatar da kansa a matsayin shugaban riko na Hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, bayan wa’adin watanni 1 ya dakatar da wanda ake tuhuma da wanda ake tuhuma na 1.

Ya roki kotun da ta bayar da sanarwar wanda ake kara na 3 ba shi da damar tantance koken wanda ake kara na 4 ta hanyar dakatar da wanda ake kara ba tare da ya fara jin ta bakin wanda ake kara ba ta hanyar da ya dace na kare kansa.

Idan za a iya tunawa majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da Barista Muhyi Magaji a matsayin shugaban hukumar tun a ranar 5 ga watan Yuli, bisa kin karbar jami’in mai mataki na 4 da aka tura ofishin sa, yayin da a ranar 26 ga wata ya ba da shawarar a kore shi, tare da gurfanar da shi, bisa zargin ya kawo takardar jabu ta rashin lafiya, sai dai kusan wata 7 da faruwar al’amarin har ya zuwa yau ba ace ufam ba, walau daga majalisa ko kuma gwamnatin Kano.

nigerian news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp