fidelitybank

Muhuyi ya shigar da kara ya na kalubantar tsige shi da gwamnati Kano ta yi

Date:

Shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimin Gado ya shigar da kara a gaban kotun masana’antu ta kasa da ke Abuja, ya na kalubalantar tsige shi da gwamnatin Ganduje ta yi a Kano.

A karar da Magaji ya shigar, gwamnatin jihar Kano ce tun a farko da ake tuhuma, yayin da aka saka sunayen manyan Lauyan jihar da majalisar dokokin jihar Kano da Akanta-Janar na jihar Kano da Barista Mahmud Balarabe da kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano a matsayin wadanda ake tuhuma na 2, 3, 4, 5 da 6, bi da bi.

Ya na rokon kotu da ta tantance ko ta duba da sashe na 8,15(i),(g), da (h), dokar hukumar korafe-korafen Jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008. Cikin 36 na (1) na kundin tsarin mulki kasa na shekara 1999.

Wanda ake kara na 1 zai iya sa wanda ake kara na 3 ya tantance koken wanda ake kara na hudu ta hanyar dakatar da wanda ake kara daga matsayinsa na shugaban hukumar kare kararrakin jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, neman hakkin mai da’awar na sauraron adalci.

Barista Muhuyi Magaji ta bakin lauyoyinsa, karkashin jagorancin Muhammad Ibrahim Tola, ya kuma bukaci kotun masana’antu ta kasa da ta tantance ko ta hanyar sashe na 4 (a), 5, da 6 na dokar hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta 2008.

Wanda ake kara na 5 ya na da hurumin ci gaba da gabatar da kansa a matsayin shugaban riko na Hukumar korafe-korafen jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta Jihar Kano, bayan wa’adin watanni 1 ya dakatar da wanda ake tuhuma da wanda ake tuhuma na 1.

Ya roki kotun da ta bayar da sanarwar wanda ake kara na 3 ba shi da damar tantance koken wanda ake kara na 4 ta hanyar dakatar da wanda ake kara ba tare da ya fara jin ta bakin wanda ake kara ba ta hanyar da ya dace na kare kansa.

Idan za a iya tunawa majalisar dokokin jihar Kano ta dakatar da Barista Muhyi Magaji a matsayin shugaban hukumar tun a ranar 5 ga watan Yuli, bisa kin karbar jami’in mai mataki na 4 da aka tura ofishin sa, yayin da a ranar 26 ga wata ya ba da shawarar a kore shi, tare da gurfanar da shi, bisa zargin ya kawo takardar jabu ta rashin lafiya, sai dai kusan wata 7 da faruwar al’amarin har ya zuwa yau ba ace ufam ba, walau daga majalisa ko kuma gwamnatin Kano.

daily sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...
X whatsapp