fidelitybank

Muhuyi Magaji ya daukaka kara a kan dakatarwar da kotu ta yi masa

Date:

Shugaban Hukumar Korafe-korafen Jama’a da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Jihar Kano, PCACC, Muhuyi Magaji, wanda kotun da’ar ma’aikata ta CCT ta dakatar, ya daukaka kara kan hukuncin.

Kotun mutum uku karkashin jagorancin Mai shari’a Danladi Umar, a ranar Alhamis a Abuja, ta bayar da umarnin dakatar da Magaji daga mukaminsa sakamakon zargin da hukumar Code of Conduct Bureau, CCB ta fifita a kansa.

Da yake yanke hukuncin, Mai shari’a Umar, wanda ya yi watsi da bukatar Magaji, ya ce kotun na da hurumin sauraron karar.

Ya umurci Gwamna Abba Yusuf na jihar Kano da sakataren gwamnatin jihar da su nada jami’in da ya fi dacewa ya karbi ragamar shugabancin hukumar har sai an saurari karar da kuma yanke hukunci.

Bai gamsu da hukuncin ba, Magaji, ta bakin lauyansa, Adeola Adedipe, ya garzaya kotun daukaka kara dake Abuja.

A cikin sanarwar daukaka kara mai kwanan wata kuma Adedipe ya shigar a ranar 5 ga Afrilu, babban lauyan ya bayar da dalilai guda biyar da ya sa a amince da daukaka karar sannan kotun daukaka kara ta soke hukuncin da CCT ta yanke.

Ya kara da cewa, CCT ya yi kuskure a doka, a lokacin da ta hana wanda yake karewa hakkinsa na yin shari’a ta gaskiya, sauraron shari’a, da kuma hakkin a ce ba shi da laifi, ta hanyar ba shi umarnin ya sauka daga mukaminsa na shugaban PCACC, ta yadda ta tantance laifinsa. a matakin interlocutory.

Ya bayyana hukuncin a matsayin “rashin adalci.”

Ya ci gaba da cewa kotun ta yi kuskure a shari’a lokacin da ta yanke hukuncin cewa Magaji zai iya yin kutse ga shaidun CCB a PCACC, duk da cewa ba a gabatar da wata hujja ta zahiri da za ta goyi bayan irin wannan hasashe ba.

latest news in nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp