Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido, ya gargadi jam’iyyarsa ta PDP cewa, idan har ta yi sake, za ta ci gaba da zama a gidan jiya na zama kadaici a zaben 2023.
Vanguard ta rawaito cewa, Alhaji Sule Lamido ya na cewa, muddin jam’iyyar PDP ta gagara shawo kan batun jam’iyar, to tabbas jam’iyar APC na iya cigaba da mulkin kasar nan.
Ganin yadda ake ta surutu kussan kullum a kan inda za a kai tikitin PDP, Sule ya ce, sai jam’iyya ta na nan daram, sannan za a fara maganar wa za a ba takara.
Tsohon gwamnan ya na ganin idan PDP ta sha kashi a zaben 2023, Najeriya ta tashi daga aiki kenan. A na sa ra’ayin jam’iyyarsa kadai za ta iya rike kasar. “Idan mu ka gaza samun mulki a zaben 2023, watakila karshen Najeriya ta zo kenan.” – Sule Lamido.