Gwamna Nasir El-Rufai ya shawarci ’yan Najeriya da su ci gaba da aiwatar da darussa na sadaukarwa, kula da marasa galihu, zurfafa tunani na ruhi, da soyayya ga dukkan bil’adama, ba tare da la’akari da kabila ko addini ba, kamar yadda aka yi a lokacin Azumi.
Gwamnan ya bayar da shawarar ne a sakonsa na Easter ranar Lahadi a Kaduna.
El-Rufai, wanda ya bayyana ‘yan Najeriya a matsayin masu imani, ya shawarci ‘yan kasa kada su bari zuciyar su ya yi sanyi.
“Mu rike junanmu a cikin amana tare da yin addu’ar samun zaman lafiya a kasarmu. Mu yi iyakar kokarinmu wajen ganin mun samar da zaman lafiya a tsakanin al’ummarmu, mu yi watsi da rigingimu a kasarmu,” in ji Gwamnan Kaduna.
El-Rufai ya kuma yi nuni da cewa Ista na nuni da nasarar bege kan yanke kauna da kuma tabbatar da cewa duhu ba zai iya rusa tsare-tsare da nufin Allah ba.