Gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi, ya yi kira ga al’ummar jihar da su gudanar da addu’o’i na musamman domin fuskantar kalubalen tsaro a Najeriya.
Mohammed ya yi wannan kiran ne a cikin sakonsa na fatan alheri a bikin Eid-el-Maulud na 2022 (maulidin Annabi Muhammad SAW) ranar Asabar.
Ya kuma bukaci al’umma da su yi amfani da Sallar Mauludi wajen yin tunani da kuma tantance kansu don sanin irin alakar da suka yi da mahaliccinsu da sauran ‘yan uwansu a cikin shekara daya da ta gabata tare da gyara inda ya dace.
Gwamnan ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su ci gaba da zaman lafiya da juna duk da bambancin kabilanci da addini da siyasa.
Ya kara jaddada kudirin gwamnatinsa na tabbatar da doka da oda, ya kuma kara da cewa gwamnati tare da hadin gwiwar hukumomin tsaro sun dauki dukkan matakan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al’ummar jihar.
“Ya kamata dukkanmu mu yi addu’o’i na musamman domin samun zaman lafiya a jiharmu musamman da kasa baki daya dangane da matsalolin tsaro da ake fuskanta a sassan kasar nan.