fidelitybank

Mu ne muka kashe sojojin Nijar – Al-Qaeda

Date:

Reshen yankin Sahel na ƙungiyar al-Qaeda ya yi iƙirarin ɗaukar alhakin kashe sojojin Nijar 17 cikin wani hari da ‘yan bindigar masu iƙirarin jihadi suka kai a yankin Tillaberi.

Ƙungiyar Jamaat Nusrat al-Islam wal-Muslimin (JNIM) ta ɗauki alhakin cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Telegram ranar 17 ga watan Agusta.

Ta ce maharan sun yi wa sojojin kwanton-ɓauna tsakanin garuruwan Boni da Torodi da ke kusa da iyakar Nijar da Burkina Faso a ranar Talata da ta wuce.

Ƙungiyar ta wallafa hotuna huɗu na motoci da makamai da suka sace bayan harin.

Rundunar sojin Nijar ta ce sojojin 17 aka kashe tare da raunata wasu 20, tana mai cewa ta kashe 100 daga cikin maharan yayin da suke ƙoƙarin guduwa.

Sanarwar ta JNIM na zuwa ne yayin da ƙungiyar Ecowas ke cewa tana shirin tura dakarun soja Nijar ɗin don tilasta wa sojojin mulkin ƙasar dawo da mulkin farar hula bayan kifar da gwamnatin Mohamed Bazoum a watan Yuli.

tribune news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp