fidelitybank

Mu na zargin gwamnatin tarayya da yin sulhu da ƴan bindiga – Gwamnan Zamfara

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci gwamnatin tararraya ta gudanar da cikakken bincike game da wata tattaunawar sulhu ta sirri da ake yi da ƴan bindiga a jihar.

Rahotanni sun bayyana cewar tawagar wasu hukumomi da Gwamnatin Tarayya ta aika sun fara tattaunawa da ƙungiyoyin ƴan bindiga ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

A ranar Litinin Kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar da wata sanarwa, ta nuna rashin jin dadin yadda wasu hukumomin Gwamnatin Tarayya suka gana da ƴan bindiga ba tare da tuntuɓar gwamnati da hukumonin tsaron jihar ba.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewar: ”Gwamna Dauda Lawal ya buƙaci gwamnatin tarayya ta fayyace wannan mataki na wasu hukumominta, wanda ya ci karo da ƙudurin gwamnatin jihar na amfani da ƙarfi kan ƴan bindigar.

Ya ƙara da kira ga gwamnati ta binciki wannan lamari, wanda tamkar zagon ƙasa ne ga yunƙurin gwamnatin jihar na yaƙar ƴan fashin daji.

Gwamnatin Zamfara ta ce ta samu rahoton yadda jami`an gwamnatin tarayya suka gana da ƙungiyoyin ƴan fashin daji a yankunan Birnin Magaji da Maradun da Mun haye da Bawo da kuma Bagege.

“Yunƙurin yin sulhun da ƴan fashi da tsohuwar gamnatin jihar ta yi a baya bai yi tasiri ba. Ya kamata mu ɗauki darasi daga kura-kuran baya tare da ɗaukar sabbin hanyoyin dawo da zaman lafiya Zamfara.”

“Kasancewar yaƙi da fashin daji na cikin manyan ƙudurorin gwamnatin jihar Zamfara, ba za mu lamunci duk wani abu da zai kawo cikas ga hakan ba.”

Muna buƙatar Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki nan take ta hanyar dakatar da duk wata tattaunawa da ake yi da ƴan fashin daji a Zamafra, domin hakan zagon ƙasa ne ga matakan da ake ɗauka.” In ji sanarwar.

www.nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp