fidelitybank

Mu na zargin gwamnatin tarayya da yin sulhu da ƴan bindiga – Gwamnan Zamfara

Date:

Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya buƙaci gwamnatin tararraya ta gudanar da cikakken bincike game da wata tattaunawar sulhu ta sirri da ake yi da ƴan bindiga a jihar.

Rahotanni sun bayyana cewar tawagar wasu hukumomi da Gwamnatin Tarayya ta aika sun fara tattaunawa da ƙungiyoyin ƴan bindiga ba tare da sanin gwamnatin jihar ba.

A ranar Litinin Kakakin gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar da wata sanarwa, ta nuna rashin jin dadin yadda wasu hukumomin Gwamnatin Tarayya suka gana da ƴan bindiga ba tare da tuntuɓar gwamnati da hukumonin tsaron jihar ba.

Sanarwar ta kuma ƙara da cewar: ”Gwamna Dauda Lawal ya buƙaci gwamnatin tarayya ta fayyace wannan mataki na wasu hukumominta, wanda ya ci karo da ƙudurin gwamnatin jihar na amfani da ƙarfi kan ƴan bindigar.

Ya ƙara da kira ga gwamnati ta binciki wannan lamari, wanda tamkar zagon ƙasa ne ga yunƙurin gwamnatin jihar na yaƙar ƴan fashin daji.

Gwamnatin Zamfara ta ce ta samu rahoton yadda jami`an gwamnatin tarayya suka gana da ƙungiyoyin ƴan fashin daji a yankunan Birnin Magaji da Maradun da Mun haye da Bawo da kuma Bagege.

“Yunƙurin yin sulhun da ƴan fashi da tsohuwar gamnatin jihar ta yi a baya bai yi tasiri ba. Ya kamata mu ɗauki darasi daga kura-kuran baya tare da ɗaukar sabbin hanyoyin dawo da zaman lafiya Zamfara.”

“Kasancewar yaƙi da fashin daji na cikin manyan ƙudurorin gwamnatin jihar Zamfara, ba za mu lamunci duk wani abu da zai kawo cikas ga hakan ba.”

Muna buƙatar Gwamnatin Tarayya ta ɗauki mataki nan take ta hanyar dakatar da duk wata tattaunawa da ake yi da ƴan fashin daji a Zamafra, domin hakan zagon ƙasa ne ga matakan da ake ɗauka.” In ji sanarwar.

thisdaynews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp