Hukumar lafiya ta duniya, WHO, ta ce Masar ta yi nasarar kawar da cutar zazzaɓin cizon sauro – maleriya – lamarin da ya jawo wa ƙasar yabo sosai.
“Cutar maleriya ta daɗe a ƙasar, amma yanzu an samu nasarar yaƙarta baki ɗaya,” kamar yadda shugaban WHO, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya bayyana a wata sanarwa.
Kusan shekara 100 da suka gabata ne ƙasar ta ƙaddamar da yaƙi da cutar ta maleriya, wadda take kashe aƙalla mutum 600,000 duk shekara a duniya, mafi yawa a ƙasashen nahiyar Afirka.
A sanarwar, WHO, ta yaba wa ƙasar Masar da mutanenta bisa ƙoƙarin da suka yi wajen “yaƙi da cutar wadda ta kasance a nahiyar tun shekaru aru-aru.
Bayan yaƙi da cutar, kafin WHO ta ayyana nasarar ƙasar, sai da ta gamsu da shirinta na kare sake komawar cutar.