Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Sokoto, ta yi kira ga Hukumar Alhazai ta kasa (NAHCON) da ta kara wa’adin biyan kudin Hajjin 2025 da makwanni biyu don baiwa sauran alhazai damar kammala biyansu.
Mukaddashin babban sakataren hukumar, Ladan Ibrahim ne ya yi wannan roko yayin da yake yiwa manema labarai karin haske kan matakin da jihar ta dauka na shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin bana.
“Tare da tsawaitawa, mutane da yawa za su iya kammala biyan su cikin lokaci, don tabbatar da cewa babu wanda ya rasa,” in ji Ibrahim.
Ya bayyana damuwarsa kan yadda da dama daga cikin maniyyatan da suka fito daga yankunan karkara na kokawa kan cika wa’adin da aka diba musu, ya kuma jaddada cewa karin wa’adin zai ba da damar yin cikakken rajistar wuraren da aka ware.
“A da, an bar mu mu biya ko da bayan Ramadan. Tare da tsawaita ɗan gajeren lokaci, muna da tabbacin cewa duk wuraren da aka ware za a yi rajista gabaɗaya,” in ji shi.
Hukumar ta NAHCON ta ware wa jihar Sokoto guraben aikin Hajji guda 5,216, amma Ibrahim ya bayyana cewa maniyyata 1,700 ne kawai suka fara ajiya.
Duk da kalubalen da ake fuskanta, ya ba da tabbacin cewa hukumar ta shirya kusan kashi 70% domin gudanar da aikin hajji, bayan da ta samu masauki a Makka da Madina, da kammala hidimar abinci, da kuma shirya wuraren jin dadi ga mahajjata.
Ya kuma bayyana cewa tuni jihar Sokoto ta turawa hukumar NAHCON sama da naira biliyan 5, wanda ya hada da kudaden ajiya na farko da kuma wasu kudade.
Bugu da kari, ya kara da cewa, ana ci gaba da tattaunawa da gwamnatin jihar domin bayar da tallafin kudi ga maniyyata, kwatankwacin tallafin da aka bayar a bara.