fidelitybank

Mu na rokon Gwamnatin Tinubu ta janye zargin da ake yi wa Kanu – Lauyoyinsa

Date:

Lauyoyin Nnamdi Kanu, jagoran ƴan awaren Biyafara, sun buƙaci gwamnatin Najeriya ta janye zargin ta’addanci da ake masa, ko kuma a bayar da shi beli domin ya samu isasshen lokacin shirya kare kansa.

Lauyoyin sun bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, inda suka ƙara da cewa wanda suke karewa yana tsare ne a wajen hukumar DSS.

Aloy Ejimakor, shi ne jagoran lauyoyin na Kanu, ya ce, “Inda ake cigaba da tsare shi a ofishin DSS ba shi da kyau sosai, kuma ba zai samu natsuwar shiryawa domin kare kansa a kotu ba a wajen.”

Lauyan ya ƙara cewa dalilin da ya sa Kanu ya buƙaci wancan mai shari’ar da ke sauraron shari’ar ta janye shi ne tunanin da yake cewa ana tauye masa haƙƙinsa na ɗan Adam, kuma ba a ba shi damar kare kansa.

Shi ma barista Nnaemeka Ejiofor, ya ce abin da Kanu yake buƙata a yi masa ba raina kotu ba ne, illa kawai yana amfani da damar da kundin tsarin mulkin ƙasar ya tanada masa.

Shi ma wani daga cikin lauyoyin nasa, Jude Uguwanyi ya alaƙanta cigaba da fama da matsalar tsaro da ake yi a kudu maso gabas da cigaba da tsare Kanu da gwamnati ke yi.Mu

sani ahmad

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp