fidelitybank

Mu na neman Mutane 8 ciki harda Farfesa wanda suka kashe mana jami’ai – Sojoji

Date:

Shalkwatar tsaro ta kasa ta ce, tana neman wasu mutum takwas ruwa a jallo saboda zargin su da hannu a kisan sojoji 17 a yankin Okuama da ke jihar Delta.

Daraktan yaɗa labaran tsaro Manjo Janar Edward Buba ne ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka yi a hedikwatar tsaron da ke Abuja, babban birnin Najeriya.

Shalkwatar tsaron ta fitar da sunayen mutanen takwas ranar Alhamis da suka haɗa da farfesa Ekpekpo Arthur da Andaowei Dennis Bakriri da Akevwru Daniel Omotegbo sai Akata Malawa David da Sinclear Oliki da Clement Ikolo Ogenerukeywe da Reuben Baru sai kuma Igoli Ebi.

Buba ya yi kira ga masu ruwa da tsaki da sarakunan gargajiya a faɗin Najeriya musamman a yankin Neja Delta su taimaka wa sojoji wajen zaƙulo waɗanda aka ayyana ana neman ruwa a jallo.

A ranar 14 ga watan Maris ne wasu ɓata-gari suka afka wa sojojin da ke aikin wanzar da zaman lafiya tsakanin al’umomin yankunan Okuoma da Okoloba inda suka kashe su.

A ranar Laraba ne kuma aka yi jana’izar sojojin a maƙabartar sojoji ta ƙasa da ke Abuja inda shugaba Bola Tinubu ya halarta tare da wasu manyan jami’an gwamnati.

vanguard newspaper nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp