fidelitybank

Mu na neman dan kasar Birtaniya ruwa a jallo bisa yunkurin kifar da gwamnatin Tinubu – ‘Yan Sanda

Date:

Rundunar ‘yan sanda ta bayyana neman wani Andrew Wynne dan kasar Birtaniya da ake nema ruwa a jallo, bisa zarginsa da yunkurin kifar da gwamnatin shugaba Bola Tinubu.

Wynne kuma ana kiransa Andrew Povich ko Drew Povey.

Rundunar ta ce ta kaddamar da wani cikakken bincike na musamman kan yadda wasu sojojin hayar kasashen waje suka kulla makarkashiyar kifar da gwamnatin da aka zaba ta dimokradiyya a Najeriya.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan a hedikwatar rundunar da ke Abuja a ranar Litinin.

Adejobi ya ce dan Burtaniya ya yi hayar fili ne a Labor House, Abuja, don yin wani kantin sayar da litattafai na ‘Iva Valley Bookshop’ sannan ya kafa ‘STARS of Nations Schools’ a matsayin fakewa da ayyukansa na zagon kasa.

Adejobi ya kuma shaida wa manema labarai cewa shaidun rubuce-rubuce da ikirari sun nuna cewa Wynne ya ba da umarni tare da sanya ido kan yadda zanga-zangar ta watan Agusta ke gudana.

Babban jami’in ‘yan sandan ya kara da cewa, dan kasar waje ya bayar da shawarwarin kudi da kuma yadda ake gudanar da aiki domin samun sauyin tsarin mulkin da bai dace ba a Najeriya.

Ya ce, “Rundunar ‘yan sandan Najeriya ta fara gudanar da cikakken bincike kan ayyukan wani dan kasar waje da kuma ‘yan ta’adda masu yin zagon kasa da ke kulla makarkashiyar kawo cikas ga zababbiyar gwamnatin dimokaradiyya a Najeriya ta hanyar sauya tsarin mulkin da bai dace ba da kuma kitsa tashin hankali a fadin kasar.

“Bayan tattara bayanan sirri da hadin gwiwa da sauran jami’an tsaro, an kama wasu mutane tara wadanda ake zargi da samun tallafin kudade daga wasu majiyoyin waje domin tada zaune tsaye a kasar.

“Bincike na farko ya nuna cewa sun kitsa tare da ba da gudummawa ga zanga-zangar tarzoma, yada labaran karya, da kuma yin wasu ayyukan da ba su dace ba don haifar da rikici da kuma tabbatar da haramtacciyar makircinsu na hambarar da gwamnatin dimokuradiyya.”

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp