fidelitybank

Mu na murna da kama riƙaƙƙen Ɗan Daba Gundura – Mazauna Unguwar wƊorayi

Date:

Mazauna yankin unguwar Ɗorayi dake ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, na nuna murnar su bisa nasarar kama ƙasurgumin Ɗan Daban nan da ya addaɓe su mai laƙani da Gundura .

Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta ce, ta kama wani ƙasurgumin ɗandaba da ake nema ruwa a jallo mai suna Inuwa Zakari wanda aka fi sani da Gundura.

Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce an kuma samu nasarar kama wasu ɓata-gari 14 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a samamen da suka yi ranakun 25 da 27 ga watan Oktoba.

Kiyawa ya ce ɗandaban ya addabi al’ummar kwaryar birnin Kano saboda irin laifuka da yake aikatawa.

“Ya kuma kasance wanda ya haɗa baki da wasu wajen kai hari kan kwamandan ƴan bijilanti har suka raunata shi ta hanyar cire masa hannu, da kuma lalata motar ƴan sanda a wani lamari na daban,” in ji Kiyawa.

Kakakin ƴan sandan ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan waɗanda ake zargin a sashen binciken manyan laifuka na rundunar, inda daga bisani za a tura su zuwa kotu domin su fuskanci hukunci.

Ya ce rundunar ba za ta lamunci ayyukan ƴandaba ba da kuma aikata sauran laifuka a jihar.

Sai dai shugaban tsaron yankin Ɗorayi, Dr Abdullahi Ɗan Fodio, ya shaidawa manema labarai cewa, dama Gundura ya gundure su, kama shi babban abun farin ciki ne a gare su.

punch news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...
X whatsapp