Mazauna yankin unguwar Ɗorayi dake ƙaramar hukumar Gwale a jihar Kano, na nuna murnar su bisa nasarar kama ƙasurgumin Ɗan Daban nan da ya addaɓe su mai laƙani da Gundura .
Rundunar ƴan sanda a jihar Kano ta ce, ta kama wani ƙasurgumin ɗandaba da ake nema ruwa a jallo mai suna Inuwa Zakari wanda aka fi sani da Gundura.
Wata sanarwa da mai magana da yawun ƴan sandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce an kuma samu nasarar kama wasu ɓata-gari 14 waɗanda ake zargi da aikata laifuka daban-daban a samamen da suka yi ranakun 25 da 27 ga watan Oktoba.
Kiyawa ya ce ɗandaban ya addabi al’ummar kwaryar birnin Kano saboda irin laifuka da yake aikatawa.
“Ya kuma kasance wanda ya haɗa baki da wasu wajen kai hari kan kwamandan ƴan bijilanti har suka raunata shi ta hanyar cire masa hannu, da kuma lalata motar ƴan sanda a wani lamari na daban,” in ji Kiyawa.
Kakakin ƴan sandan ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan waɗanda ake zargin a sashen binciken manyan laifuka na rundunar, inda daga bisani za a tura su zuwa kotu domin su fuskanci hukunci.
Ya ce rundunar ba za ta lamunci ayyukan ƴandaba ba da kuma aikata sauran laifuka a jihar.
Sai dai shugaban tsaron yankin Ɗorayi, Dr Abdullahi Ɗan Fodio, ya shaidawa manema labarai cewa, dama Gundura ya gundure su, kama shi babban abun farin ciki ne a gare su.