Afirka ta Kudu ta yi maraba da batun tsagaita wuta da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira da a gaggauta a Gaza.
Cikin wata kuri’a da aka kada a ranar Litinin, kwamitin ya bukaci a tsagaita wuta har zuwa karshen watan Ramadan, wanda zai kare nan da makonni biyu.
Cikin wata sanarwa da ministar harkokin wajen Afirka ta Kudu Naledi Pandorin, ta fitar,ta ce kasarta ta ji dadin yarjejeniya, to amma ta yi kira da a samu tsagaita wuta ta dindindin.
Ta ce,” Yanzu alhakin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin duniyar ne ya tabbatar da cewa ba a samu wata matsala a wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta ba.”
Yarjejeniyar tsagaita wutar wadda a cikinta aka yi kiran da a saki mutanen da aka tsare da su, ta samu cikas a lokuta da dama. In ji BBC.
Wannan ne dai karon farko da kwamitin ya yi wannan kiran tun bayan fara yakin.
Amurka dai ta kauracewa kada kuri’ar, yayin da sauran kasashe 14 na kwamitin kuma suka kada kuri’ar amincewarsu da batun tsagaita wutar.