fidelitybank

Mu na maraba da tsagaita wuta a Gaza – Afrika ta Kudu

Date:

Afirka ta Kudu ta yi maraba da batun tsagaita wuta da kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya yi kira da a gaggauta a Gaza.

Cikin wata kuri’a da aka kada a ranar Litinin, kwamitin ya bukaci a tsagaita wuta har zuwa karshen watan Ramadan, wanda zai kare nan da makonni biyu.

Cikin wata sanarwa da ministar harkokin wajen Afirka ta Kudu Naledi Pandorin, ta fitar,ta ce kasarta ta ji dadin yarjejeniya, to amma ta yi kira da a samu tsagaita wuta ta dindindin.

Ta ce,” Yanzu alhakin kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin duniyar ne ya tabbatar da cewa ba a samu wata matsala a wannan yarjejeniya ta tsagaita wuta ba.”

Yarjejeniyar tsagaita wutar wadda a cikinta aka yi kiran da a saki mutanen da aka tsare da su, ta samu cikas a lokuta da dama. In ji BBC.

Wannan ne dai karon farko da kwamitin ya yi wannan kiran tun bayan fara yakin.

Amurka dai ta kauracewa kada kuri’ar, yayin da sauran kasashe 14 na kwamitin kuma suka kada kuri’ar amincewarsu da batun tsagaita wutar.

legit.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp