Najeriya ta yi kira da a samar da ƙasashen Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu, inda ta ce hakan ne zai wanzar da zaman lafiya a yankin.
Ƙasar ta bayyana haka ne a lokacin da take maraba da tsagaita wuta da aka yi a Gaza tsakanin Isra’ila da Hamas.
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Najeriya, Kimiebi Ebienfa ne ya bayyana haka a zantawarsa da tashar Channels mai zaman kanta a Najeriya.
“Najeriya na kira ga dukkan ɓangarori su haɗa kai domin tabbatar da an cimma sauran matakan yarjejeniyar tsagaita wutar, sannan Najeriya na kira da a samar da ƙasashen biyu na Isra’ila da Falasɗinu masu cin gashin kansu a matsayin hanya ɗaya tilo da za a tabbatar da zaman lafiya a yankin,” in ji Ebienfa.