Gwamnatin Najeriya ta jajanta wa Koriya ta Kudu game da hatsarin jigrin sama da ya kashe mutum 179 ranar Lahadi.
Cikin wata sanarwa, Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya ta bayyana alhininta ga iyalan waɗanda hatsarin ya shafa, tare da tausaya wa gwamnatinn ƙasar.
Lamarin ya faru ne lokacin da jirgin ƙirar Boeing 737-800, wanda ke komawa ƙasar daga birnin Bangkok na Thailand, ya yi ƙoƙarin sauka a filin jirgi na Muan International Airport da ke kudancin Koriya ta Kudu.
Jirgin ya zarce tare da sauka daga titinsa kuma ya tunkuyi wani bango, abin da ya sa ya kama da wuta nan take. Mutum 179 ne suka mutu cikin 181 da ke cikinsa, inda biyu suka tsira da raunuka.
Tuni hukumomi suka ayyana makokin kwana bakwai.