fidelitybank

Mu na gudanar da bincike a kan yawan ma’aikatan gwamnati – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya ce, gwamnatinsa na gudanar da gagarumin bincike kan yawan ma’aikatan gwamnatin tarayya.

Mista Tinubu ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da shugaban Bankin Duniya Mr. Ajay Banga da ya kai masa ziyara a fadarsa da ke Abuja

Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale ya fitar, shugaba Tinubu ya ce ”za mu gudanar da gagarumin bincike, tare da nazarin tsarin albashin ma’aikatan gwamnatin tarayya”.

”Ban amince da adadin mutanen da ke kan rajistar albashin ma’aikatan gwamnatin tarayyara ba, a baya lokacin da nake gwamna na fuskanci irin wannan matsala”.

Tinubu ya ce gwamnatinsa a shirye take don toshe duk wata kafa da kuɗaɗen gwamnati ke zurarewa.

Sanarawar ta ce za a gudanar da binciken ne domin gyara tsarin aikin gwamnati a ƙasar, tare da sauya dabi’un ‘yan ƙasar da kuma wayar da kan jama’a.

Haka kuma shugaban ya ce a yanzu haka gwamnatinsa na gudanar da wani binciken ƙwaƙaf a babban bankin ƙasar CBN.

Makonni bayan rantsar Bola Tinubu a matsayin shugaban ƙasa, ya dakatar da gwamnan babban bankin ƙasar Godwin Emefiele, bisa zargin aikata ba daidai ba.

legit

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...
X whatsapp