Shugaban ƙasa Bola Tinubu, ya ce, gwamnatinsa na gudanar da gagarumin bincike kan yawan ma’aikatan gwamnatin tarayya.
Mista Tinubu ya bayyana hakan a lokacin da yake ganawa da shugaban Bankin Duniya Mr. Ajay Banga da ya kai masa ziyara a fadarsa da ke Abuja
Cikin wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Ajuri Ngelale ya fitar, shugaba Tinubu ya ce ”za mu gudanar da gagarumin bincike, tare da nazarin tsarin albashin ma’aikatan gwamnatin tarayya”.
”Ban amince da adadin mutanen da ke kan rajistar albashin ma’aikatan gwamnatin tarayyara ba, a baya lokacin da nake gwamna na fuskanci irin wannan matsala”.
Tinubu ya ce gwamnatinsa a shirye take don toshe duk wata kafa da kuɗaɗen gwamnati ke zurarewa.
Sanarawar ta ce za a gudanar da binciken ne domin gyara tsarin aikin gwamnati a ƙasar, tare da sauya dabi’un ‘yan ƙasar da kuma wayar da kan jama’a.
Haka kuma shugaban ya ce a yanzu haka gwamnatinsa na gudanar da wani binciken ƙwaƙaf a babban bankin ƙasar CBN.
Makonni bayan rantsar Bola Tinubu a matsayin shugaban ƙasa, ya dakatar da gwamnan babban bankin ƙasar Godwin Emefiele, bisa zargin aikata ba daidai ba.