Manyan ƙasashen Turai huɗu sun bayyana goyon bayansu ga ƙasashen Larabawa kan shirin zaman lafiyar Gaza.
Ministocin harkokin wajen ƙasashen Faransa da Jamus da Italiya da Birtaniya sun yi maraba da shirin a matsayin abu na zahirin – saɓanin shawarar Amurka da Isra’ila da suka riga suka yi watsi da shirin.
Shirin ƙasashen Larabawar ya tanadi sake gina Gaza cikin shekara biyar, ƙarƙashin kulawar ƙwararrun Falasɗinawa, kafin lokacin da gwamnatin Falasɗinawa za ta karɓe iko da shirin.
Ƙasar Masar ce ta jagoranci ɓullo da shirin, a wani mataki na martani kan shawarar shugaban Amurka Donald Trump na kwashe al’ummar Gaza domin sake gina yankin.