Ƙungiyar bunƙasa tattalin arziƙin ƙasashen Afirka ta Yamma, ECOWAS ta bayyana goyon bayanta ga Najeriya da sauran ƙasashen ƙungiyar kan zargin ɗaukar nauyin ta’addanci da Jamhuriyar Nijar ta yi.
Shugaban mulkin sojin Nijar, Abdourahamane Tchiani dai ya zargi Najeriya da haɗa baki da Faransa domin tayar da ‘rikici’ a ƙasarsa.
A sanarwar da ECOWAS ta fitar, ta ce zarge-zargen na Nijar babu ƙamshin gaskiya a ciki.
“Najeriya ta daɗe tana taimakon ƙasashen Afirka wajen wanzar da zaman lafiya, ba ma a yankin Afirka ta yamma kaɗai ba. Irin nasarorin da dakarun haɗin gwiwa na MNJTF, wadda Najeriya ke kan gaba wajen ɗaukar nauyi ke samu, na ƙara nuna jajircewar ƙasar a nahiyar.
“Wannan ya sa ECOWAS ta ƙaryata zargin cewa wannan ƙasa mai ƙoƙarin jiɓintar lamarin wasu ce za ta ɗauki nauyin ta’addanci,” kamar yadda sanarwar ta nuna.
A ƙarshe ECOWAS ta yi kira ga ƙasashen yankin da su haɗa kai domin wanzar da zaman lafiya a yankin tare da nesantar jifar juna da zarge-zarge.