fidelitybank

Mu na goyon bayan auren Matan Neja – Kwamitin Malamai

Date:

Kwamitin malaman addinin musulunci na Najeriya ya goyi bayan auren marayu 100 da kakakin majalisar dokokin jihar Neja ya ƙuduri aniyar ɗaukar nauyi.

Cikin wata takarda da kwamitin ya fitar, mai ɗauke da sa hannun shugaban kwamitin, Malam Aminu Inuwa Muhammad da sakatarensa, Engr Basheer Adamu Aliyu, sun ce abin da kakakin majalisar ke shirin yi abin a yaba ne, ba na kushewa ba.

Kwamitin ya ce duba da matsalar tsaro da matsin tattalin arziki da wasu yankunan arewacin Najeriya ke fuskanta, ɗaukar nauyin aure wani nau’i ne na tallafa wa marasa ƙarfi

”A shekarun baya-bayan nan jihar Neja da wasu jihohin arewa maso yammacin Najeriya na fama da matsalar tsaro da ‘yan bindiga masu satar mutane domin neman kuɗin fansa, lamarin da ya shafi rayuwar mutanen yankin, iyalai da dama sun rasa iyayensu, kan haka ne shugabannin al’ummar yankin ke ƙoƙarin magance musu wahalhalun da suke fuskanta ta ɓangarori daban-daban, kamar yadda kakakin majalisar dokokin Neja ya yi yunƙurin yi”, in ji sanarwar.

”A matsayinmu na musulmi muna ƙoƙarin yin abubuwa kamar yadda shari’a ta tanadar, su kansu ‘yan matan sun zaɓi su yi aure, a maimakon su faɗa karuwanci ko a yi safararsu zuwa Turai kamar yadda wasu da ba su da hali ke yi don rage wa kansu matsin rayuwa”, kamar yadda sanarwar ta yi bayani.

Kwamitin malaman addinin musuluncin ya ce abin da ministar ta yi bai dace ba.

”Abin da minista ta yi nuna wariya ne da wargaza abu mai kyau da rashin ƙwarewar aiki da kuma ƙabilanci, domin kundin tsarin mulkin Najeriya ya amince da ‘yancin addinin tare da amincewa ta shari’ar musulunci da ta amince da aure”, in ji sanarwar.

A makon da ya gabata ne dai ministar mata ta Najeriya ta kai ƙarar kakakin majalisar dokokin jihar Nejan zuwa ga babban sifeton ‘yan sandan ƙasar bisa zarginsa da tilasta aurar da ‘yan matan da ta ce masu ƙananan shekaru ne.

Ministar ta ce idan taimakon ‘yan matan kakakin majalisar ke son yi, me zai hana ya ɗauki nauyin karatunsu, ko ya basu jari domin su tsaya da ƙafafunsu, a maimakon yi musu aure.

To sai dai ɗan majalisar ya kare matakin da cewa taimakon yaran ya yi, yana mai cewa galibinsu marayu ne waɗansa suka rasa iyayensu sakamakon matsalar tsaro da wasu sassan jihar ke fuskanta.

legit nigeria news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp