fidelitybank

Mu na gargadin jihohi 11 su kula da madatsar ruwan da Kamaru za ta saki – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta gargaɗi ƴan ƙasar da su kasance cikin shirin shigowar ruwa daga dam ɗin Lagdo na ƙasar Kamaru.

Darakta-Janar na Hukumar Nigeria Hydrological Service Agency (NIHSA), Umar Mohammed, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Sai dai ya buƙaci ƴan Najeriya su kwantar da hankalinsu, inda ya ce ba za a samu mummunar ambaliya ba a Najeriya saboda buɗe dam ɗin.

Sai dai ya ƙara da cewa jihohin Adamawa da Taraba da Kogi da Nasarawa da Benue da Anambra da Bayelsa da Delta da Edo da Kuros Riba da Rivers suna buƙatar fara shirin ko ta kwana domin rage illar ambaliyar idan ta auku.

Dam ɗin Lagdo da yake arewacin Kamaru yana girman 586 km2.

Wata ƙididdiga daga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta nuna cewa da aka sakok ruwan dam ɗin a shekarar 2022, ya jawo mummunar ambaliya, inda mutum 603 suka mutu, sannan sama da mutum miliyan 1.4 suka rasa muhallansu, sannan wasu 2,400 suka jikkata.

Haka ambaliyar ta 2022 ta ɓarnata gidaje 82,035 da hekta 332,327 na gonaki.

A watan Oktoban 2023 ne Majalisar Dattawa ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta waiwayi batun gina madatsar ruwa na Dasin Hausa da sauransu domin su riƙa tare ruwan dam ɗin na Lagdo na Kamaru idan ya malalo, kamar yadda muka kalato daga Daily Trust.

punch news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp