fidelitybank

Mu na gargadin jihohi 11 su kula da madatsar ruwan da Kamaru za ta saki – Gwamnati

Date:

Gwamnatin Tarayya ta gargaɗi ƴan ƙasar da su kasance cikin shirin shigowar ruwa daga dam ɗin Lagdo na ƙasar Kamaru.

Darakta-Janar na Hukumar Nigeria Hydrological Service Agency (NIHSA), Umar Mohammed, ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.

Sai dai ya buƙaci ƴan Najeriya su kwantar da hankalinsu, inda ya ce ba za a samu mummunar ambaliya ba a Najeriya saboda buɗe dam ɗin.

Sai dai ya ƙara da cewa jihohin Adamawa da Taraba da Kogi da Nasarawa da Benue da Anambra da Bayelsa da Delta da Edo da Kuros Riba da Rivers suna buƙatar fara shirin ko ta kwana domin rage illar ambaliyar idan ta auku.

Dam ɗin Lagdo da yake arewacin Kamaru yana girman 586 km2.

Wata ƙididdiga daga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta nuna cewa da aka sakok ruwan dam ɗin a shekarar 2022, ya jawo mummunar ambaliya, inda mutum 603 suka mutu, sannan sama da mutum miliyan 1.4 suka rasa muhallansu, sannan wasu 2,400 suka jikkata.

Haka ambaliyar ta 2022 ta ɓarnata gidaje 82,035 da hekta 332,327 na gonaki.

A watan Oktoban 2023 ne Majalisar Dattawa ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta waiwayi batun gina madatsar ruwa na Dasin Hausa da sauransu domin su riƙa tare ruwan dam ɗin na Lagdo na Kamaru idan ya malalo, kamar yadda muka kalato daga Daily Trust.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ƙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haƙƙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riƙaƙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ‘yan...

Fadar shugaban ƙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp