fidelitybank

Mu na gargadi a kan harajin VAT – ASUU

Date:

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i, (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya yi gargaɗi kan ƙarin harajin kayayyaki na VAT da aka gabatar a cikin kudirin dokar gyaran haraji ta gwamnati.

Dole ya bayyana haka ne a wata hira da aka yi da shi a tashar talabijin ta Channels TV, inda ya soki gwamnatin tarayya da ‘yan majalisa bisa goyon bayan kudirin ba tare da tuntuɓar masu ruwa da tsaki ba.

Ya ce akwai abubuwa da dama da aka haɗa a cikin kudirin da bai kamata a sanya su ba.

Mista Osodeke ya yi bayanin cewa ƙarin VAT zai ƙara wa ‘yan Najeriya wahala, musamman ma waɗanda har yanzu ke fama da tasirin cire tallafin man fetur da kuma karyewar darajar Naira.

Osodeke yace “Ina ganin abinda ya kamata mu kalla a cikin wannan kudirin shi ne yadda zai shafi talakan Najeriya. Na ji mutane daga sassa daban-daban suna cewa muna goyon baya, ba mu yarda ba,

Yace “VAT haraji ne akan masu amfani da kayayyaki, wato ‘yan Najeriya. Don haka, idan aka ƙara VAT a yau, ba masu ƙirƙirar kayayyaki zai shafa ba; zai shafi masu amfani da kayayyakin ne saboda abinda masu ƙirƙirar kayayyakin za su yi shi ne su ƙara farashi a kan kayan da ake sayarwa,” .

Shugaban ASUU ya kuma gargaɗi gwamnatin tarayya da kada ta soke Asusun Tallafin Ilimin Manyan Makarantu (TETFund) don maye gurbinsa da sabon Asusun Lamunin Ilimi na Najeriya (NELFUND), yana mai cewa wannan matakin na iya lalata tsarin jami’o’in gwamnati a ƙasar.

TETFund ya taka rawa wajen inganta manyan makarantu a Najeriya sama da shekaru 30.

Shugaban ƙungiyar malaman ya ba da shawarar cewa gwamnati ta binciki hanyoyin samun kuɗi na daban don NELFUND, kamar ware wani kaso daga Harajin Kayayyaki da Ayyuka (VAT), maimakon amfani da kuɗaɗen TETFund daga harajin kamfanoni.

punch news paper today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp